伊斯兰宝库
80

Abasa

سورة عبس

He frowned42节经文 麦加章

Translated by Abubakar Mahmoud Gumi

بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيمِ

1

بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيمِ عَبَسَ وَتَوَلَّىٰ

Yã game huska kuma ya jũya bãya.

2

أَنْ جَاءَهُ الْأَعْمَىٰ

Sabõda makãho yã je masa.

3

وَمَا يُدْرِيكَ لَعَلَّهُ يَزَّكَّىٰ

To, me ya sanar da kai cẽwa watakila shi ne zai tsarkaka.

4

أَوْ يَذَّكَّرُ فَتَنْفَعَهُ الذِّكْرَىٰ

Ko ya tuna, dõmin tunãwar ta amfane shi?

5

أَمَّا مَنِ اسْتَغْنَىٰ

Amma wanda ya wadãtu da dũkiya.

6

فَأَنْتَ لَهُ تَصَدَّىٰ

Sa'an nan kai kuma ka ɗora bijira zuwa gare shi!

7

وَمَا عَلَيْكَ أَلَّا يَزَّكَّىٰ

To, me zai cũce ka idan bai tsarkaka ba?

8

وَأَمَّا مَنْ جَاءَكَ يَسْعَىٰ

Kuma, amma wanda ya zomaka yana gaugãwa.

9

وَهُوَ يَخْشَىٰ

Alhãli shĩ yanã jin tsõrõn Allah.

10

فَأَنْتَ عَنْهُ تَلَهَّىٰ

Kai kuma kã shagala ga barinsa!

11

كَلَّا إِنَّهَا تَذْكِرَةٌ

A'aha! Lalle ne, wannan tunãtarwa ce.

12

فَمَنْ شَاءَ ذَكَرَهُ

Sabõda wanda ya so ya tunaShi (Allah).

13

فِي صُحُفٍ مُكَرَّمَةٍ

(Tunãtarwa ce) ta cikin littafai abãban girmamãwa,

14

مَرْفُوعَةٍ مُطَهَّرَةٍ

Abãban ɗaukakãwa, abãban tsarkakẽwa.

15

بِأَيْدِي سَفَرَةٍ

A cikin hannãyen mala'iku marubũta.

16

كِرَامٍ بَرَرَةٍ

Mãsu daraja, mãsu ɗã'a ga Allah.

17

قُتِلَ الْإِنْسَانُ مَا أَكْفَرَهُ

An la'ani mutum (kafiri). Mẽ yã yi kãfircinsa!

18

مِنْ أَيِّ شَيْءٍ خَلَقَهُ

Daga wane abu, (Allah) Ya halitta shi?

19

مِنْ نُطْفَةٍ خَلَقَهُ فَقَدَّرَهُ

Daga ɗigon maniyyi, Ya halitta shi sa'an nan Ya ƙaddarã shi (ga halaye).

20

ثُمَّ السَّبِيلَ يَسَّرَهُ

Sa'an nan, hanyarsa ta fita Ya sauƙaƙe masa.

21

ثُمَّ أَمَاتَهُ فَأَقْبَرَهُ

Sa'an nan, Ya matar da shi sai Ya sanya shi a cikin kabari.

22

ثُمَّ إِذَا شَاءَ أَنْشَرَهُ

Sa'an nan, idan Ya so lalle ne zai tãyar da shi.

23

كَلَّا لَمَّا يَقْضِ مَا أَمَرَهُ

Haƙĩƙa bai i da aikata abin da Allah Ya umurce shi ba (lõkacin sanya shi a cikin kabari).

24

فَلْيَنْظُرِ الْإِنْسَانُ إِلَىٰ طَعَامِهِ

To, mutum ya dũba zuwa ga abincinsa.

25

أَنَّا صَبَبْنَا الْمَاءَ صَبًّا

Lalle ne Mũ, Mun zuo ruwa, zubõwa.

26

ثُمَّ شَقَقْنَا الْأَرْضَ شَقًّا

Sa'an nan, Muka tsattsãge ƙasa tsattsagewa.

27

فَأَنْبَتْنَا فِيهَا حَبًّا

Sa'an nan, Muka tsirar da ƙwaya, a cikinta.

28

وَعِنَبًا وَقَضْبًا

Da inabi da ciyãwa.

29

وَزَيْتُونًا وَنَخْلًا

Da zaitũni da itãcen dabĩno.

30

وَحَدَائِقَ غُلْبًا

Da lambuna, mãsu yawan itãce.

31

وَفَاكِهَةً وَأَبًّا

Da 'yã'yan itãcen marmari, da makiyãyã ta dabbõbi.

32

مَتَاعًا لَكُمْ وَلِأَنْعَامِكُمْ

Domin jin dãɗi a gare ku, ku da dabbobinku.

33

فَإِذَا جَاءَتِ الصَّاخَّةُ

To, idan mai tsãwa (busa ta biyu) ta zo.

34

يَوْمَ يَفِرُّ الْمَرْءُ مِنْ أَخِيهِ

Rãnar da mutum yake gudu daga ɗan'uwansa.

35

وَأُمِّهِ وَأَبِيهِ

Da uwarsa da ubansa.

36

وَصَاحِبَتِهِ وَبَنِيهِ

Da mãtarsa da ɗiyansa.

37

لِكُلِّ امْرِئٍ مِنْهُمْ يَوْمَئِذٍ شَأْنٌ يُغْنِيهِ

Ga kõwane mutum daga cikinsu, a rãnar nan akwai wani sha'ani da ya ishe shi.

38

وُجُوهٌ يَوْمَئِذٍ مُسْفِرَةٌ

Wasu huskõki, a rãnar nan, mãsu haske ne.

39

ضَاحِكَةٌ مُسْتَبْشِرَةٌ

Mãsu dãriya ne, mãsu bushãra.

40

وَوُجُوهٌ يَوْمَئِذٍ عَلَيْهَا غَبَرَةٌ

Wasu huskõki, a rãnar nan, akwai ƙũra a kansu.

41

تَرْهَقُهَا قَتَرَةٌ

Baƙi zai rufe su.

42

أُولَٰئِكَ هُمُ الْكَفَرَةُ الْفَجَرَةُ

Waɗannan sũ ne kãfirai fãjirai (ga ayyukansu).

Islamic Vault

Quran Explorer

一个全面的在线资源,用于阅读和学习神圣古兰经,提供多种翻译、音译和著名诵读者的音频诵读。

这部经典,其中毫无可疑,是敬畏者的向导。

古兰经 2:2

功能

  • 音频诵读
  • 多种翻译
  • 音译
  • 114章
  • 6,236节经文

© 2026 伊斯兰宝库。保留所有权利。

以对真主之书的敬畏和关怀而构建

免责声明: 虽然我们力求准确,但请与可靠的伊斯兰学者和来源核实重要的宗教信息。本平台仅供教育目的。