伊斯兰宝库
79

An-Naazi'aat

سورة النازعات

Those who drag forth46节经文 麦加章

Translated by Abubakar Mahmoud Gumi

بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيمِ

1

بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيمِ وَالنَّازِعَاتِ غَرْقًا

Ina rantsuwa da mala'iku mãsu fisgar rãyuka (na kafirai) da ƙarfi.

2

وَالنَّاشِطَاتِ نَشْطًا

Da mãsu ɗibar rãyuka (na mũminai) da sauƙi a cikin nishãɗi.

3

وَالسَّابِحَاتِ سَبْحًا

Da mãsu sauka daga sama da umurnin Allah kamar suna iyo.

4

فَالسَّابِقَاتِ سَبْقًا

Sa'an nan, su zama mãsu gaugãwa (da umurnin Allah) kamar suna tsẽre.

5

فَالْمُدَبِّرَاتِ أَمْرًا

Sa, an nan, su kasance masu shirya gudanar da umurni.

6

يَوْمَ تَرْجُفُ الرَّاجِفَةُ

Rãnar da mai girgiza abũbuwa (bũsar farko) zã ta kaɗa.

7

تَتْبَعُهَا الرَّادِفَةُ

Mai biyar ta (bũsa ta biyu) nã biye.

8

قُلُوبٌ يَوْمَئِذٍ وَاجِفَةٌ

Wasu zukãta, a rãnar nan, mãsu jin tsõro ne.

9

أَبْصَارُهَا خَاشِعَةٌ

Alhãli idãnunsu na ƙasƙantattu.

10

يَقُولُونَ أَإِنَّا لَمَرْدُودُونَ فِي الْحَافِرَةِ

Sunã cẽwa "Ashe lalle zã a iya mayar da mu a kan sãwunmu?

11

أَإِذَا كُنَّا عِظَامًا نَخِرَةً

"Ashe, idan muka zama ƙasusuwa rududdugaggu?"

12

قَالُوا تِلْكَ إِذًا كَرَّةٌ خَاسِرَةٌ

Suka ce: "Waccan kam kõmãwa ce, tãɓaɓɓiya!"

13

فَإِنَّمَا هِيَ زَجْرَةٌ وَاحِدَةٌ

To, ita kam, tsãwa guda kawai ce.

14

فَإِذَا هُمْ بِالسَّاهِرَةِ

Sai kawai gã su a bãyan ƙasa.

15

هَلْ أَتَاكَ حَدِيثُ مُوسَىٰ

Shin, lãbãrin Mũsã ya zo maka?

16

إِذْ نَادَاهُ رَبُّهُ بِالْوَادِ الْمُقَدَّسِ طُوًى

A lõkacin da Ubangijinsa Ya kirãye shi, a cikin kwari mai tsarki, wato Duwã?

17

اذْهَبْ إِلَىٰ فِرْعَوْنَ إِنَّهُ طَغَىٰ

Ka tafi zuwa ga Fir'auna, lalle ne shi, ya ƙẽtare haddi.

18

فَقُلْ هَلْ لَكَ إِلَىٰ أَنْ تَزَكَّىٰ

"Sai ka ce masa, Kõ zã ka so ka tsarkaka.

19

وَأَهْدِيَكَ إِلَىٰ رَبِّكَ فَتَخْشَىٰ

"Kuma in shiryar da kai zuwa ga Ubangijinka domin ka ji tsoronSa?"

20

فَأَرَاهُ الْآيَةَ الْكُبْرَىٰ

Sai ya nũna masa ãyar nan mafi girma.

21

فَكَذَّبَ وَعَصَىٰ

Sai ya ƙaryata, kuma ya sãɓa (umurni),

22

ثُمَّ أَدْبَرَ يَسْعَىٰ

Sa'an nan ya jũya bãya, yanã tafiya da sauri.

23

فَحَشَرَ فَنَادَىٰ

Sai ya yi gayya, sa'an nan ya yi kira.

24

فَقَالَ أَنَا رَبُّكُمُ الْأَعْلَىٰ

Sai ya ce: "Nĩ ne Ubangijinku mafi ɗaudaka."

25

فَأَخَذَهُ اللَّهُ نَكَالَ الْآخِرَةِ وَالْأُولَىٰ

Sabõda haka Allah Ya kama shi, dõmin azãbar maganar ƙarshe da ta farko.

26

إِنَّ فِي ذَٰلِكَ لَعِبْرَةً لِمَنْ يَخْشَىٰ

Lalle ne, a cikin wannan haƙiƙa akwai abin kula ga wanda yake tsõron Allah.

27

أَأَنْتُمْ أَشَدُّ خَلْقًا أَمِ السَّمَاءُ ۚ بَنَاهَا

Shin, kũ ne mafi wuyar halitta ko sama? Allah Ya gina ta.

28

رَفَعَ سَمْكَهَا فَسَوَّاهَا

Ya ɗaukaka rufinta, sa'an nan Ya daidaita ta.

29

وَأَغْطَشَ لَيْلَهَا وَأَخْرَجَ ضُحَاهَا

Kuma Ya duhuntar da darenta, kuma Ya fitar da hantsinta.

30

وَالْأَرْضَ بَعْدَ ذَٰلِكَ دَحَاهَا

Kuma, ƙasa a bayan haka Ya mulmula ta.

31

أَخْرَجَ مِنْهَا مَاءَهَا وَمَرْعَاهَا

Ya fitar da ruwanta daga gare ta da makiyãyarta.

32

وَالْجِبَالَ أَرْسَاهَا

Da duwatsu, Yã kafe ta.

33

مَتَاعًا لَكُمْ وَلِأَنْعَامِكُمْ

Domin jiyarwa dãɗi a gare ku, kuma ga dabbõbinku.

34

فَإِذَا جَاءَتِ الطَّامَّةُ الْكُبْرَىٰ

To, idan uwar masĩfu, mafi girma, ta zo.

35

يَوْمَ يَتَذَكَّرُ الْإِنْسَانُ مَا سَعَىٰ

Rãnar da mutum zai yi tunãnin abin da ya aikata.

36

وَبُرِّزَتِ الْجَحِيمُ لِمَنْ يَرَىٰ

Kuma, a bayyana Jahĩm ga mai gani.

37

فَأَمَّا مَنْ طَغَىٰ

To, amma wanda ya yi girman kai.

38

وَآثَرَ الْحَيَاةَ الدُّنْيَا

Kuma, ya zãɓi rãyuwa ta kusa, (wato dũniya).

39

فَإِنَّ الْجَحِيمَ هِيَ الْمَأْوَىٰ

To, lalle ne Jahĩm, ita ce makõma.

40

وَأَمَّا مَنْ خَافَ مَقَامَ رَبِّهِ وَنَهَى النَّفْسَ عَنِ الْهَوَىٰ

Kuma, amma wanda ya ji tsõron tsayi a gaba ga Ubangijinsa, kuma ya kange kansa daga son rai.

41

فَإِنَّ الْجَنَّةَ هِيَ الْمَأْوَىٰ

To, lalle ne Aljanna ita ce makõma.

42

يَسْأَلُونَكَ عَنِ السَّاعَةِ أَيَّانَ مُرْسَاهَا

Sunã tambayar ka game da sa'a, wai yaushe ne matabbatarta?

43

فِيمَ أَنْتَ مِنْ ذِكْرَاهَا

Me ya haɗã ka da ambatonta?

44

إِلَىٰ رَبِّكَ مُنْتَهَاهَا

Zuwa ga Ubangijinka ƙarshen al'amarinta yake.

45

إِنَّمَا أَنْتَ مُنْذِرُ مَنْ يَخْشَاهَا

Kai mai gargaɗi kawai ne ga mai tsõron ta.

46

كَأَنَّهُمْ يَوْمَ يَرَوْنَهَا لَمْ يَلْبَثُوا إِلَّا عَشِيَّةً أَوْ ضُحَاهَا

Kamar sũ a rãnar da zã su gan ta, ba su zauna ba fãce a lõkacin marẽce ko hantsinsa.

Islamic Vault

Quran Explorer

一个全面的在线资源,用于阅读和学习神圣古兰经,提供多种翻译、音译和著名诵读者的音频诵读。

这部经典,其中毫无可疑,是敬畏者的向导。

古兰经 2:2

功能

  • 音频诵读
  • 多种翻译
  • 音译
  • 114章
  • 6,236节经文

© 2026 伊斯兰宝库。保留所有权利。

以对真主之书的敬畏和关怀而构建

免责声明: 虽然我们力求准确,但请与可靠的伊斯兰学者和来源核实重要的宗教信息。本平台仅供教育目的。