105

Al-Fil

سورة الفيل

The Elephant5 ayat Makkiyah

Translated by Abubakar Mahmoud Gumi

بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيمِ

1

بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيمِ أَلَمْ تَرَ كَيْفَ فَعَلَ رَبُّكَ بِأَصْحَابِ الْفِيلِ

Ashe, ba ka ga yadda Ubangijinka Ya aikata ga mutanen giwa ba?

2

أَلَمْ يَجْعَلْ كَيْدَهُمْ فِي تَضْلِيلٍ

Ashe, bai sanya kaidinsu a cikin ɓata ba?

3

وَأَرْسَلَ عَلَيْهِمْ طَيْرًا أَبَابِيلَ

Kuma Ya sako, a kansu, wasu tsuntsãye, jama'a-jama'a.

4

تَرْمِيهِمْ بِحِجَارَةٍ مِنْ سِجِّيلٍ

Suna jifar su da wasu duwatsu na yumɓun wuta.

5

فَجَعَلَهُمْ كَعَصْفٍ مَأْكُولٍ

Sa'an nan Ya sanya su kamar karmami wanda aka cinye?