1

Al-Faatiha

سورة الفاتحة

The Opening7 Verse Mekkanisch

Translated by Abubakar Mahmoud Gumi

1

بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيمِ

Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai.

2

الْحَمْدُ لِلَّهِ رَبِّ الْعَالَمِينَ

Godiya ta tabbata ga Allah, Ubangijin halittu;

3

الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيمِ

Mai rahama, Mai jin ƙai;

4

مَالِكِ يَوْمِ الدِّينِ

Mai nuna Mulkin Rãnar Sakamako.

5

إِيَّاكَ نَعْبُدُ وَإِيَّاكَ نَسْتَعِينُ

Kai muke bauta wa, kuma Kai muke neman taimakonKa.

6

اهْدِنَا الصِّرَاطَ الْمُسْتَقِيمَ

Ka shiryar da mu ga hanya madaidaiciya.

7

صِرَاطَ الَّذِينَ أَنْعَمْتَ عَلَيْهِمْ غَيْرِ الْمَغْضُوبِ عَلَيْهِمْ وَلَا الضَّالِّينَ

Hanyar waɗanda Ka yi wa ni'ima, ba waɗanda aka yi wa fushi ba, kuma ba ɓatattu ba.