99

Az-Zalzala

سورة الزلزلة

The Earthquake8 آیات مدنی

Translated by Abubakar Mahmoud Gumi

بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيمِ

1

بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيمِ إِذَا زُلْزِلَتِ الْأَرْضُ زِلْزَالَهَا

Idan aka girgiza ƙasa, girgizawarta.

2

وَأَخْرَجَتِ الْأَرْضُ أَثْقَالَهَا

Kuma ƙasa ta fitar da kayanta, masu nauyi.

3

وَقَالَ الْإِنْسَانُ مَا لَهَا

Kuma mutum ya ce "Mẽ neya same ta?"

4

يَوْمَئِذٍ تُحَدِّثُ أَخْبَارَهَا

A rãnar nan, zã ta faɗi lãbãrinta.

5

بِأَنَّ رَبَّكَ أَوْحَىٰ لَهَا

cewa Ubangijinka Ya yi umurni zuwa gare ta.

6

يَوْمَئِذٍ يَصْدُرُ النَّاسُ أَشْتَاتًا لِيُرَوْا أَعْمَالَهُمْ

A rãnar nan mutane za su fito dabam-dabam domin a nuna musu ayyukansu.

7

فَمَنْ يَعْمَلْ مِثْقَالَ ذَرَّةٍ خَيْرًا يَرَهُ

To, wanda ya aikata (wani aiki) gwargwadon nauyin zarra, na alheri, zai gan shi.

8

وَمَنْ يَعْمَلْ مِثْقَالَ ذَرَّةٍ شَرًّا يَرَهُ

Kuma wanda ya aikata gwargwadon nauyin zarra na sharri, zai gan shi.