Islamic Vault
80

Abasa

سورة عبس

He frowned42 ayat Makkiyyah

Translated by Abubakar Mahmoud Gumi

بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيمِ

1

بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيمِ عَبَسَ وَتَوَلَّىٰ

Yã game huska kuma ya jũya bãya.

2

أَنْ جَاءَهُ الْأَعْمَىٰ

Sabõda makãho yã je masa.

3

وَمَا يُدْرِيكَ لَعَلَّهُ يَزَّكَّىٰ

To, me ya sanar da kai cẽwa watakila shi ne zai tsarkaka.

4

أَوْ يَذَّكَّرُ فَتَنْفَعَهُ الذِّكْرَىٰ

Ko ya tuna, dõmin tunãwar ta amfane shi?

5

أَمَّا مَنِ اسْتَغْنَىٰ

Amma wanda ya wadãtu da dũkiya.

6

فَأَنْتَ لَهُ تَصَدَّىٰ

Sa'an nan kai kuma ka ɗora bijira zuwa gare shi!

7

وَمَا عَلَيْكَ أَلَّا يَزَّكَّىٰ

To, me zai cũce ka idan bai tsarkaka ba?

8

وَأَمَّا مَنْ جَاءَكَ يَسْعَىٰ

Kuma, amma wanda ya zomaka yana gaugãwa.

9

وَهُوَ يَخْشَىٰ

Alhãli shĩ yanã jin tsõrõn Allah.

10

فَأَنْتَ عَنْهُ تَلَهَّىٰ

Kai kuma kã shagala ga barinsa!

11

كَلَّا إِنَّهَا تَذْكِرَةٌ

A'aha! Lalle ne, wannan tunãtarwa ce.

12

فَمَنْ شَاءَ ذَكَرَهُ

Sabõda wanda ya so ya tunaShi (Allah).

13

فِي صُحُفٍ مُكَرَّمَةٍ

(Tunãtarwa ce) ta cikin littafai abãban girmamãwa,

14

مَرْفُوعَةٍ مُطَهَّرَةٍ

Abãban ɗaukakãwa, abãban tsarkakẽwa.

15

بِأَيْدِي سَفَرَةٍ

A cikin hannãyen mala'iku marubũta.

16

كِرَامٍ بَرَرَةٍ

Mãsu daraja, mãsu ɗã'a ga Allah.

17

قُتِلَ الْإِنْسَانُ مَا أَكْفَرَهُ

An la'ani mutum (kafiri). Mẽ yã yi kãfircinsa!

18

مِنْ أَيِّ شَيْءٍ خَلَقَهُ

Daga wane abu, (Allah) Ya halitta shi?

19

مِنْ نُطْفَةٍ خَلَقَهُ فَقَدَّرَهُ

Daga ɗigon maniyyi, Ya halitta shi sa'an nan Ya ƙaddarã shi (ga halaye).

20

ثُمَّ السَّبِيلَ يَسَّرَهُ

Sa'an nan, hanyarsa ta fita Ya sauƙaƙe masa.

21

ثُمَّ أَمَاتَهُ فَأَقْبَرَهُ

Sa'an nan, Ya matar da shi sai Ya sanya shi a cikin kabari.

22

ثُمَّ إِذَا شَاءَ أَنْشَرَهُ

Sa'an nan, idan Ya so lalle ne zai tãyar da shi.

23

كَلَّا لَمَّا يَقْضِ مَا أَمَرَهُ

Haƙĩƙa bai i da aikata abin da Allah Ya umurce shi ba (lõkacin sanya shi a cikin kabari).

24

فَلْيَنْظُرِ الْإِنْسَانُ إِلَىٰ طَعَامِهِ

To, mutum ya dũba zuwa ga abincinsa.

25

أَنَّا صَبَبْنَا الْمَاءَ صَبًّا

Lalle ne Mũ, Mun zuo ruwa, zubõwa.

26

ثُمَّ شَقَقْنَا الْأَرْضَ شَقًّا

Sa'an nan, Muka tsattsãge ƙasa tsattsagewa.

27

فَأَنْبَتْنَا فِيهَا حَبًّا

Sa'an nan, Muka tsirar da ƙwaya, a cikinta.

28

وَعِنَبًا وَقَضْبًا

Da inabi da ciyãwa.

29

وَزَيْتُونًا وَنَخْلًا

Da zaitũni da itãcen dabĩno.

30

وَحَدَائِقَ غُلْبًا

Da lambuna, mãsu yawan itãce.

31

وَفَاكِهَةً وَأَبًّا

Da 'yã'yan itãcen marmari, da makiyãyã ta dabbõbi.

32

مَتَاعًا لَكُمْ وَلِأَنْعَامِكُمْ

Domin jin dãɗi a gare ku, ku da dabbobinku.

33

فَإِذَا جَاءَتِ الصَّاخَّةُ

To, idan mai tsãwa (busa ta biyu) ta zo.

34

يَوْمَ يَفِرُّ الْمَرْءُ مِنْ أَخِيهِ

Rãnar da mutum yake gudu daga ɗan'uwansa.

35

وَأُمِّهِ وَأَبِيهِ

Da uwarsa da ubansa.

36

وَصَاحِبَتِهِ وَبَنِيهِ

Da mãtarsa da ɗiyansa.

37

لِكُلِّ امْرِئٍ مِنْهُمْ يَوْمَئِذٍ شَأْنٌ يُغْنِيهِ

Ga kõwane mutum daga cikinsu, a rãnar nan akwai wani sha'ani da ya ishe shi.

38

وُجُوهٌ يَوْمَئِذٍ مُسْفِرَةٌ

Wasu huskõki, a rãnar nan, mãsu haske ne.

39

ضَاحِكَةٌ مُسْتَبْشِرَةٌ

Mãsu dãriya ne, mãsu bushãra.

40

وَوُجُوهٌ يَوْمَئِذٍ عَلَيْهَا غَبَرَةٌ

Wasu huskõki, a rãnar nan, akwai ƙũra a kansu.

41

تَرْهَقُهَا قَتَرَةٌ

Baƙi zai rufe su.

42

أُولَٰئِكَ هُمُ الْكَفَرَةُ الْفَجَرَةُ

Waɗannan sũ ne kãfirai fãjirai (ga ayyukansu).

Islamic Vault

Quran Explorer

Sumber dalam talian yang komprehensif untuk membaca dan mengkaji Al-Quran dengan pelbagai terjemahan, transliterasi, dan bacaan audio daripada qari terkenal.

Kitab ini tidak ada keraguan padanya, petunjuk bagi orang-orang yang bertakwa.

Al-Quran 2:2

Ciri-ciri

  • Bacaan Audio
  • Pelbagai Terjemahan
  • Transliterasi
  • 114 Surah
  • 6,236 Ayat

© 2026 Islamic Vault. Hak cipta terpelihara.

Dibina dengan penghormatan dan ketelitian untuk Kitabullah

Dibangunkan oleh Medita Development

Penafian: Walaupun kami berusaha untuk ketepatan, sila sahkan maklumat agama penting dengan ulama Islam dan sumber yang sahih. Platform ini adalah untuk tujuan pendidikan.