1
بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيمِ قُلْ أَعُوذُ بِرَبِّ النَّاسِ
Ka ce "Ina nẽman tsari ga Ubangijin mutãne."
Quran
سورة الناسMankind • 6 ayat • MakkiyyahTranslated by Abubakar Mahmoud Gumi
بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيمِ
بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيمِ قُلْ أَعُوذُ بِرَبِّ النَّاسِ
Ka ce "Ina nẽman tsari ga Ubangijin mutãne."
مَلِكِ النَّاسِ
"Mamallakin mutane."
إِلَٰهِ النَّاسِ
"Abin bautãwar mutãne."
مِنْ شَرِّ الْوَسْوَاسِ الْخَنَّاسِ
"Daga sharrin mai sanya wasuwãsi, mai ɓoyewa."
الَّذِي يُوَسْوِسُ فِي صُدُورِ النَّاسِ
"Wanda ke sanya wasuwãsi a cikin ƙirãzan mutane."
مِنَ الْجِنَّةِ وَالنَّاسِ
"Daga aljannu da mutane."